25 Maris 2026 - 23:19
Source: ABNA24
Hizbullah Ta Harba Makamai Masu Linzami 30 A Cikin 'Yan Sa'o'i Da Suka Gabata Kan Isra’ila

Jaridar Yedioth Ahronoth ta bayar rahoton cewa tun daga safiyar yau, gwagwarmaya kasar ta Lebanon ta ci gaba da kai hare-hare ba tare sassautawa ba a kan wuraren sahyoniyawa.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Kungiyar Hizbullah ta tilastawa jiragen yakin Isra'ila ja da baya kungiyar Hizbullah ta ce ta kai hari kan wani jirgin yakin Isra'ila da makamai masu linzami yayin da suke kai hari a kudancin Lebanon, lamarin da ya tilasta masa ja da baya.

A lokaci guda da kungiyar Hizbullah ta yi a Lebanon ta fitar da wata sanarwa da ke cewa, ta kai hari kan tankunan Merkava guda 8 da wata Buldoza ta Isra'ila nau’in D9 a yankin Al-Tayba ta hanyar amfani da makamai masu linzami.

Hizbullah: A karo na uku, Mujahidan gwagwarmaya sun kai hari kan taron sojojin abokan gaba na Isra'ila a cikin aikin hari na AlTaiba tare da wani jirgin sama mara matuki. Sannan ta kai wani harin makami mai linzami a Naharia

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha